Kotun Shari’ar Musulunci ta Upper Sharia Court Shahuci da ke Kano, ƙarƙashin jagorancin Alƙali Abdu Abdullahi Wayyah, ta yanke hukunci kan wani matashi da aka samu da laifin dukan wani mutum har ya samu karaya. Kotun ta samu matashin mai suna Hassan Abba, mazaunin unguwar Durumin Iya – Lokon Maraba, da laifin kai wa wani matashi mai suna Ibrahim Haruna hari, lamarin da ya haddasa masa karaya a mukamuki. Bayanai da suka fito daga kotun sun nuna cewa wanda aka samu da laifin na daga cikin matasan da ake kira masu sukuwa da doki a bayan Gidan Sarkin Kano, duk…
Author: Kabiru Basiru Fulatan
Read More