Daga Abbas Ibrahim Wani hari da aka kai kan wasu ’yan jarida a Kano yayin da suke dawowa daga wani taron jam’iyyar APC ya sake haifar da damuwa kan tsaron ma’aikatan kafafen yaɗa labarai a lokacin harkokin siyasa. Lamarin ya faru ne a ranar 5 ga Satumba 2026, bayan wasu ’yan jarida sun kammala ɗaukar rahoton wani taron siyasa da aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano. Rahotanni sun ce wasu da ake zargin ’yan daba ne sun far wa motar Radio Nigeria Pyramid FM da ke ɗauke da ’yan jaridar. An ce maharan sun yi…
Author: Kabiru Basiru Fulatan
Ɗan takarar gwamnan Jihar Kano na jam’iyyar Labour Party (LP), Alhaji Hamisu Santuraki, ya yi alkawarin kafa Hukumar Kula da Hayar Gidaje da ’Yan Hayar Gida, idan aka zaɓe shi a zaɓen 2027. Santuraki ya ce manufar hukumar ita ce dakile ƙarin kuɗin haya ba bisa ƙa’ida ba da kuma kare ’yan haya daga cin zarafi da sauran matsalolin da suka shafi haya. Ya bayyana hakan ne ta bakin mataimakinsa, Comrade Abbas Ibrahim, inda ya ce hukumar ba za ta sanya farashin haya iri ɗaya ga dukkan gidaje ba, sai dai ta tsara farashi bisa la’akari da wurin da gida…
Gwamnatin Ghana ta yi watsi da tayin tallafin kuɗi har cedi miliyan 20 daga kamfanin sadarwa na MTN Ghana, wanda kamfanin ya yi niyyar bayarwa domin tallafa wa ’yan Ghana da hare-haren ƙyamar baƙi suka shafa a Afirka ta Kudu. Daga Zainab Kamal Ibrahim Ma’aikatar Harkokin Wajen Ghana ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, 26 ga Agusta, 2026, inda ta ce ta lura da rahotannin kafafen yaɗa labarai kan shirin MTN na bayar da tallafin. Ranar Hausa Ta Duniya: Ana Bukatar Amfani Da Fasaha Wajen Bunƙasa Harshen Sanarwar ta ce duk…
Ana bikin Ranar Hausa ta Duniya a ranar 26 ga Agusta na kowace shekara, domin tunawa da muhimmancin harshen Hausa da kuma al’adun Hausawa. Daga Zainab Kamal Ibrahim Bikin, wanda aka fara gudanarwa a shekarar 2015, ya samo asali ne daga ƙoƙarin masu ruwa da tsaki wajen amfani da kafafen sada zumunta wajen bunƙasa harshen Hausa da yaɗa shi zuwa sassa daban-daban na duniya. Ranar Hausa ta Duniya na kuma zama wata dama ta haɗa masu magana da harshen tare da ƙarfafa ƙoƙarin kare shi daga tasirin sauye-sauyen zamani da kuma tabbatar da ci gaba da amfani da…
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PRP, Donald Duke, ya bayyana cewa iƙirarin cewa Najeriya ce ƙasa mafi arziki a Afirka “ƙarya ne”. Tsohon gwamnan Jihar Cross River ya ce a maimakon haka, Najeriya na daga cikin ƙasashe mafi talauci a nahiyar, kuma bai kamata a kira ta tattalin arziki mafi girma a Afirka bisa la’akari da jimillar mau’aunin tattalin arziki na GDP kawai ba. A wata hira da wasu ’yan jarida a Legas, Duke ya ce Najeriya ƙasa ce mai ƙarancin arziki idan aka yi la’akari da kudin shiga ga kowane ɗan ƙasa (per capita income). Ya ce har…
Daga Abbas Ibrahim Wani ɗan kishin al’umma, Hon. Adamu S. Ladan, FCAI, ya miƙa sabuwar makaranta mai ajujuwa shida ga Ƙaramar Hukumar Dandume da al’ummar Tudun Badole da ke Jihar Katsina. An gina makarantar ne domin taimakawa wajen inganta damar samun ingantaccen ilimi ga yara da matasa a yankin. An miƙa makarantar ga ƙaramar hukumar da al’ummar yankin ne a wani biki da aka gudanar a Tudun Badole ranar Juma’a. Da yake jawabi a wajen bikin, Ladan ya bayyana aikin a matsayin gudummawarsa wajen tallafa wa ilimi da ci gaban al’umma. Ya ce ilimi…
An yi kira ga Musulmi da su yi amfani da watan Rabi’ul Awwal wajen yawaita addu’o’i, ibada da ayyukan alheri domin neman kusanci da Allah. Daga Zainab Kamal Ibrahim Kiran ya fito ne daga bakin Sarkin Shanun Sarkin Maganin Gargajiya na Jihar Kano, Dr Abubakar Yunusa Mai Takama da Ma’aiki, yayin wata tattaunawa da wakiliyar MU, Zainab Kamal Ibrahim. Dr Yunusa ya bayyana Rabi’ul Awwal a matsayin wata mai muhimmanci ga al’ummar Musulmi, kasancewar watan da aka haifi Annabi Muhammad (S.A.W), yana mai cewa ya kamata Musulmi su yi amfani da lokacin wajen tunawa da rayuwarsa da koyarwarsa.…
Kwamitin Hadin Gwiwa na Jihar Kano dake Yaki da Miyagun Kwayoyi da sauran miyagun Laifuka masu alaka, ya kama tsohon Shugaban Karamar Hukumar Rogo bisa zargin shiga cikin sayarwa da kuma bai wa matasa alluran fentanyl ba bisa ka’ida ba. Daga Zainab Kamal Ibrahim Shugaban Kwamitin, Muhuyi Magaji Rimingado, ne ya bayyana hakan a cikin wata hira da wata kafar yada labarai a ranar Litinin, kamar yadda SolaceBase ta ruwaito. Rimingado ya ce an kama wanda ake zargin ne bayan kwamitin ya gudanar da binciken sirri don tabbatar da zargin da ake yi masa na sayarwa da kuma bai wa…
Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), ta ce sama da malamai 200 sun bar aikin jami’ar saboda rashin kyawun yanayin aiki da kuma gazawar aiwatar da yarjejeniyar da Gwamnatin Tarayya ta cimma da kungiyar a shekarar 2025. Daga Zainab Kamal Ibrahim Shugaban ASUU na reshen KASU, Dr Abubakar Abdullahi, ne ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai da kungiyar ta gudanar a Kaduna. Ya ce rashin aiwatar da yarjejeniyar na kara jefa malaman jami’ar cikin mawuyacin hali, lamarin da ya sa da dama daga cikinsu suka bar aikin. Saboda haka, kungiyar ta bai…
Almajirai huɗu sun mutu a Jihar Kano bayan sun ci wani kifi da ake zargin ya gurɓata, yayin da wani ɗalibi ke kwance a asibiti yana karɓar magani. Daga Zainab Kamal Ibrahim Lamarin ya faru ne a Tsangayar Malam Iliyasu Mai Tsangaya da ke Kadage Sharifai, a Ƙaramar Hukumar Ungogo ta Jihar Kano. Matan sun haɗa da Abdulfatah Mohammed mai shekaru 15, Yusuf Nuhu mai shekaru 16, Buhari Iliyasu mai shekaru 14 da Ibrahim Muhammad mai shekaru 22. Wani ɗalibi mai suna Auwalu Surajo, mai shekaru 18, ya tsira daga lamarin kuma yana samun kulawa a asibiti. A…