Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ƙi ganawa da wata tawaga ta musamman da Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya aiko zuwa Najeriya domin tattauna batun hare-haren kyamar baƙi da aka kai wa ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka a ƙasar. Daga Zainab Kamal Ibrahim Rahotanni sun bayyana cewa tawagar, ƙarƙashin jagorancin Ministan Harkokin Wajen Afirka ta Kudu, Ronald Lamola, ta isa Abuja ɗauke da saƙo daga Shugaba Ramaphosa. Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar mutuwar Mutane 107 Tare Da Jikkata 344 A Pakistan Sai dai, maimakon ganawa da Shugaba Tinubu, an buƙaci tawagar ta miƙa saƙon ga…
Author: Kabiru Basiru Fulatan
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta kama wata matashiya mai shekaru 25 da ake zargi da yanke mazakutar saurayinta a wani otal da ke unguwar Badawa a Kano. Daga Zainab Kamal Ibrahim Mai magana da yawun rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12 na ranar Litinin, bayan da suka samu rahoton abin da ya faru. Ƴan bindiga sun sace alkalin babbar kotun jihar Kebbi Ya ƙara da cewa bayan faruwar lamarin, matar ta yi ƙoƙarin kai saurayin zuwa banɗaki domin tsaftace jinin da ya zuba kafin mutanen da ke kusa suka gano…
Making ruwan sama da ambaliya ruwa sun yi sanadiyyar mutuwar mutane 107 da jikkata wasu 344, tare kuma da lalata ɗaruruwan gidaje tun daga ƙarshen watan Yuni zuwa yau a Pakistan. Daga Zainab Kamal Ibrahim Hukumar Kiyaye Afkuwar Iftila’i ta ƙasar NDMA, ta shaida wa manema labarai a ranar Lahadi cewa adadin mutanen da suka mutu sakamakon mamakon ruwan saman tun daga ƙarshen watan Yuni sun kai 107. Adadin mutanen da su ka rasu a lardin Khyber Pakhtunkhwa ya kai 55, tare da mutane 36 a yankin Punjabi. Kuma fiye da rabin mutanen sun mutu ne sakamakon rushewar…
Gwamnatin Jihar Bauchi ta musanta rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed ya amince da kayyade sadakin budurwa zuwa ₦3,000 da na bazawara zuwa ₦1,500, tana mai bayyana batun a matsayin ƙarya da aka ƙirƙira domin yaudarar jama’a. Daga Zainab Kamal Ibrahim Rahotannin, da suka bazu musamman a shafukan Facebook da TikTok, sun yi zargin cewa gwamnatin jihar ta fito da sabon tsarin kayyade sadaki, tare da cewa Sarkin Sayawa (Gum Zar) ya umarci al’ummar yankinsa su bi tsarin. Ana Zargin Wani Miji Da Saran Matarsa Da Ɗansa Da…
Wasu da ake zargin ‘yanbindiga ne sun sace wani alkalin babbar kotun Jihar Kebbi, Mai Shari’a Faruku Hassan Bunza, a gidansa da ke kan titin Zogirma a karamar hukumar Bunza kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito. Daga Zainab Kamal Ibrahim Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:00 na dare tsakanin Asabar da Lahadi, jim kadan bayan alkalin ya dawo daga wata tafiya daga jihar Sokoto. Wata majiya ta bayyana cewa maharan sun kutsa cikin gidan tare da tafiya da alkalin, yayin da suke ta harbe-harbe domin razana mutane. Ta ce babu wani daga cikin iyalansa…
Daga Abbas Ibrahim Babban Lauyan Jihar Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Barrista Abdulkarim Kabiru Maude, ya kasance cikin manyan baƙin da suka halarci bikin yaye ɗalibai karo na uku na Makarantar Blazing Star International School da ke unguwar Farawa a Kano. An gudanar da bikin ne a Salma Event Centre, inda ya haɗa iyaye, malamai, masu ruwa da tsaki a harkar ilimi da sauran baƙi domin taya ɗaliban murnar kammala karatunsu. Mamallakiyar makarantar, Hajiya Zahra Usman Bakare, ta ce an kafa makarantar ne domin samar wa yara ingantaccen ilimi tare da kyakkyawar tarbiyya, ta yadda za su zama nagartattun…
Babbar kotun jihar Kano ƙarƙashin mai Shari’a Farida Dan Baffa, ta yankewa Shu’ibu Abdulkadir, hukuncin kiss ta hanyar rataya mazaunin unguwar Farawa a ƙaramar hukumar Kumbotso, bayan ta same shi da laifin kashe Rumaisa Shuaibu mai shekaru 22 a duniya Daga Zainab Kamal Ibrahim An gurfanar da wanda ake zargin a ranar 23 ga Agustan 2025, kan laifin kisan kai, laifin da ya saɓa da Sashe na 221 na Dokar Penal Code, kamar yadda kafar yada Labarai ta Daily Nigeria ta ruwaito. A yayin shari’ar, masu gabatar da ƙara sun gabatar da shaidu uku tare da hujjoji…
An gano gawar wani ɗalibi na Jami’ar Tarayya ta Kashere (FUK) da ya ɓace kwanaki kaɗan da suka gabata a cikin wani tafkin ruwa mara gudana da ke ƙauyen Sabon Garin Yero, kusa da garin Kashere a Ƙaramar Hukumar Akko ta Jihar Gombe. Daga Zainab Kamal Ibrahim Marigayin, mai suna Enoch Sunday Maisamari, mai shekaru 28, ɗalibi ne a matakin shekara ta biyu a Sashen Microbiology na Tsangayar Kimiyya ta jami’ar. Mutane 68 Sun Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Jirgin Enugu Air Ya Yi Saukar Gaggawa A Benin Rahotanni sun bayyana cewa an ga Maisamari a karo na…
Aƙalla mutane 68 da ke cikin wani jirgin saman kamfanin Enugu Air sun tsallake rijiya da baya bayan da jirgin ya yi saukar gaggawa a filin jirgin saman Benin da ke Jihar Edo a ranar Alhamis. Daga Zainab Kamal Ibrahim Rahotanni sun ce jirgin mai lambar 5N-ENR na kan hanyarsa daga Enugu zuwa Benin, kafin ya ci gaba da tafiya zuwa Legas, lokacin da lamarin ya faru. Wata majiya daga filin jirgin, wadda ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida cewa bayan jirgin ya sauka, ya kauce daga hanyar saukar jirage tare da shiga wani yanki mai ciyayi…
Fasfon Nijeriya ya sake yin ƙasa a sabon jerin darajar fasfunan ƙasashen duniya na Henley Passport Index, inda ya sauka zuwa matsayi na 90 a duniya, yayin da ya kasance na 45 a nahiyar Afirka. Daga Zainab Kamal Ibrahim Rahoton watan Yulin 2026, wanda kamfanin Henley & Partners ya fitar, ya nuna cewa masu riƙe da fasfon Nijeriya na iya shiga ƙasashe 44 ba tare da neman biza kafin tafiya ba. Sabon matsayin ya nuna cewa Nijeriya ta yi ƙasa da matsayi ɗaya idan aka kwatanta da rahoton Afrilun 2026, inda ta kasance a matsayi na 89. Sai…