Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) reshen Jihar Kano ta yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa manufofinsa na kyautata jin daɗin ma’aikata, tare da yin kira da a ƙara tallafa wa masu karɓar fansho a jihar. Ƙungiyar ta bayyana hakan ne cikin saƙon taya murnar Babbar Sallah da shugaban riƙo na ƙungiyar, Kwamared Nura Rimin Gago, da sakataren riƙo, Kwamared Abbas Ibrahim suka sanyawa hannu. Yadda Cibiyoyin Farfesa Adamu Gwarzo Ke Samar Da Sabbin Damammaki Ga Matasan Afirka A cikin saƙon, NLC ta taya Gwamna Abba Kabir Yusuf, mataimakinsa Alhaji Murtala Sule Garo, ma’aikata, masu fansho da al’ummar Musulmi murnar…
Author: Kabiru Basiru Fulatan
Daga Musa Abdullahi Sufi A daidai lokacin da nahiyar Afirka ke neman shugabanni masu hangen nesa da za su kawo sauyi a fannonin ilimi, kirkire-kirkire, kasuwanci da ci gaban al’umma, sunan Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo na kara fitowa fili a matsayin daya daga cikin matasan da suka zamo abin koyi a nahiyar da ma duniya baki daya. Daga Arewacin Najeriya zuwa manyan cibiyoyin ilimi na duniya, Farfesa Gwarzo ya zama abin misali wajen jagoranci mai hangen nesa, bunkasa ilimi da kuma bai wa matasa damar cimma burinsu. Nasarorin da ya samu ba wai kawai na kansa ba ne, illa wata…
Kamfanin Maltina ya ƙaddamar da wani shiri na wayar da kan ɗalibai kan muhimmancin karatun kimiyya da fasaha a makarantu 30 da ke faɗin Jihar Kano, domin ƙarfafa harkar ilimi da bunƙasa makomar matasa a jihar. Wakilin kamfanin Maltina na Arewacin Najeriya, Kabiru Al-Kasim, ya bayyana cewa wannan ba shi ne karo na farko da kamfanin ke gudanar da irin wannan shiri a Kano ba, yana mai jaddada aniyar kamfanin na ci gaba da tallafa wa harkokin ilimi da ci gaban matasa. Da yake jawabi a wajen taron, Malam Sagiru Umar Dan Bare daga Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, ya…
Dan takarar Majalisar Jiha a Karamar Hukumar Tarauni, Hon. Sagir Wada Sinkin Mai Iyali, ya bayyana godiyarsa ga al’ummar Jihar Kano bisa yadda suke ci gaba da nuna goyon baya da amincewa da tsarin jam’iyyar NDC Kwankwasiyya da kuma ‘yan takararta masu kishin kasa. Hon. Sagir Wada Sinkin ya ce al’ummar Kano sun nuna cikakken goyon baya ga manufofin jam’iyyar tare da amincewa da shugabannin da suka hada da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da kuma jagoran siyasa, Peter Obi. Rikicin KCSF: An Bukaci Hadin Kan Ƙungiyoyi Domin Kare Manufofin “Kano First” Ya bayyana hakan ne yayin…
Daga Mohammed Bello Ana ci gaba da nuna damuwa kan rikicin shugabanci da ya kunno kai a cikin Dandalin Kungiyoyin Fararen Hula na Kano (KCSF), yayin da masu ruwa da tsaki ke gargadin cewa rikicin na iya kawo cikas ga manufar “Kano First” idan ba a magance shi cikin adalci da gaskiya ba. Wani masani kan bincike da tsara manufofi, Mohammed Bello, ya ce rikicin da ke cikin KCSF bai kamata a dauke shi a matsayin sabanin ra’ayi na cikin gida kawai ba, illa a kallesa a matsayin gwajin yadda kungiyar za ta iya kare martabarta da tsarin gudanarwarta. Bello,…
Daga Zainab Kamal Ibrahim Lalle na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin fitattun al’adun ado da suka yi tasiri a rayuwar Hausawa da sauran al’ummomin Musulmi, musamman a lokutan bukukuwa da shagulgula. Tun shekaru masu yawa da suka gabata, ana amfani da lalle a matsayin kayan kwalliya, tsafta da kuma nuna farin ciki a tsakanin mata Musulmi. Haka kuma, amfani da ita ya samu karɓuwa a Musulunci, inda malamai suka bayyana cewa addinin ya halatta amfani da ita cikin tsafta da ladabi. Rahotanni daga tarihin Musulunci sun nuna cewa tun a zamanin Annabi Muhammad (SAW), ana amfani da lalle…
Daga Zainab Kamal Ibrahim Akalla mata 500 ne suka hallara a unguwar Gwammaja da ke karamar hukumar Dala a jihar Kano domin gudanar da saukar karatun Alƙur’ani mai girma tare da addu’o’in neman zaman lafiya da kawo ƙarshen ayyukan daba da kashe-kashen matasa da suka addabi yankin. Jami’an EFCC Sun Kama Shugaban Hukumar Makamashi Kan Badaƙalar Naira Biliyan 500 Shugabar ƙungiyar da ta shirya taron, Hajiya Halima Musa Abdullahi, ta bayyana cewa makasudin gudanar da taron shi ne neman taimakon Allah kan matsalar rashin tsaro da kashe-kashen da ake yi wa matasa marasa laifi. Ta ce lamarin ya jefa…
DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta kama Darakta-Janar na Hukumar Makamashi ta Najeriya (ECN), Mustapha Abdullahi, bisa zargin almundahanar kuɗi. Kishi Ya Rikide Zuwa Tashin Hankali Yayin Da Mace Ta Kona Kishiyarta Da ’Ya’yanta A Kano Wata majiya daga hukumar ta EFCC ta ce an kama shi ne a Abuja, kuma a halin yanzu yana hannun hukumar domin ci gaba da bincike. Majiyar ta ce ana zargin cewa kuɗaɗen da ake binciken sun kai kusan Naira biliyan 500. Har yanzu EFCC ba ta fitar da cikakken bayani a hukumance ba, kuma…
DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta kama Darakta-Janar na Hukumar Makamashi ta Najeriya (ECN), Mustapha Abdullahi, bisa zargin almundahanar kuɗi. Kishi Ya Rikide Zuwa Tashin Hankali Yayin Da Mace Ta Kona Kishiyarta Da ’Ya’yanta A Kano Wata majiya daga hukumar ta EFCC ta ce an kama shi ne a Abuja, kuma a halin yanzu yana hannun hukumar domin ci gaba da bincike. Majiyar ta ce ana zargin cewa kuɗaɗen da ake binciken sun kai kusan Naira biliyan 500. Har yanzu EFCC ba ta fitar da cikakken bayani a hukumance ba, kuma ƙoƙarin…
DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM Wata mata mai shekara 28 mai suna Firdausi Musa tare da ’ya’yanta biyu ƙanana sun jikkata sakamakon mummunar ƙona da suka samu bayan da ake zargin kishiyarta, Maryam Muhammad, ta zuba musu fetur tare da banka musu wuta a unguwar Hotoro da ke cikin birnin Kano. Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wata hatsaniya da ta ɓarke tsakanin matan biyu, inda ake zargin Maryam ta kai harin ne cikin fushi. Makwabta sun ce sun yi gaggawar kai ɗauki bayan jin ihun waɗanda abin ya shafa, kafin a garzaya da su zuwa asibiti domin…