Author: Kabiru Basiru Fulatan

A ranar Lahadi, 12 ga watan Afrilu, 2026, an gudanar da bikin aure biyu a Masallacin Anas Bin Malik da ke unguwar Sheka Achilafiya, inda iyalai da abokai suka hallara domin shaida wannan muhimmin biki. Bikin ya hada auren Aliyu Abdullahi Idris, wanda aka fi sani da “Butter”, da Hauwa’u U. Abdullahi Alhassan. Haka kuma a wannan rana aka daura auren Khadija Abdullahi Idris da Usman Ismail. Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa Mahaifin ango da amarya, Abdullahi Idris, ya bayyana godiyarsa ga Allah bisa nasarar gudanar da bikin lafiya, tare da yaba…

Read More

Wani mummunan lamari ya auku a kan iyakar Jihar Borno da Jihar Yobe, inda rahotanni ke cewa wani hari daga sama da sojoji suka kai ya fada kan wata kasuwa ta al’umma, lamarin da ake fargabar ya hallaka fiye da mutane 50. Bisa ga bayanan da ke fitowa a hankali, an ce harin ya faru ne yayin wani samame da ake kai wa ‘yan tada kayar baya a yankin Arewa maso Gabas. Sai dai abin takaici, fararen hula sun tsinci kansu a cikin harin, wanda ya jawo asarar rayuka da raunuka masu yawa INEC ta ɗage aikin sabunta bayanan rajistar…

Read More

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta sanar da ɗage aikin sabunta rajistar masu zaɓe da ta shirya yi a duk faɗin ƙasar nan zuwa bayan babban zaɓen shekarar 2027 kamar yadda jaridar The Nation ta rawaito. An yanke wannan shawara ne bayan wani taro da hukumar ta gudanar da Kwamishinonin Zaɓe na jihohi, inda aka tattauna muhimman batutuwan da suka shafi zaɓe. Gwamnan Kano ya naɗa Bilkisu Maimota a matsayin shugabar ma’aikata ta jiha A wata sanarwa da Kwamishinan ƙasa kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu zaɓe, Mohammed Haruna, ya fitar, ya ce…

Read More

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya naɗa Hajiya Bilkisu Maimota a matsayin shugabar ma’aikata ta jihar ta dindindin. Wannan na kunshe a wata samarwa da babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan Kano,. Mustapha Muhammad ya fitar,.inda ya ce gwamnan ya sanar da haka ne a wajen bikin biyan ƴan fansho hakkunan su, karo na shida. TAFTA Ta Horar da Matasa 28,000 a Kano, Ta Samar da Aikin Yi ga 16,000 Ya ce tabbatar da Maimota a wannan lokacin ya yi daidai domin samun cigaba wajen gudanar da aikin gwamnati. Inda ya ce an tabbatar da Maimota ne bayan ta…

Read More

Cibiyar Terra Academy for the Arts (TAFTA), tare da haɗin gwiwar Mastercard, ta horar da matasa 28,000 a Jihar Kano domin ƙarfafa tattalin arziki da rage rashin aikin yi. Manajan shirin na TAFTA a Kano, Abubakar Balarabe, ya bayyana a wani taro da aka gudanar a Kano cewa shirin na haɗa koyon sana’o’i da damar samun aikin yi ko kafa kasuwanci. Ya ce an horar da matasa a fannoni daban-daban kamar animation, rubutun shiri (scriptwriting), fasaha, kasuwanci, ƙirar sauti da hasken dandalin wasan kwaikwayo, inda shirin ya shafi Kano, Lagos da Ogun. Balarabe ya bayyana cewa shirin, wanda yanzu ya…

Read More

‎Ya mai girma Shugaban Karamar Hukumar Tarauni, Hon. Ahmad Sekure a matsayina na dan karamar hukumar Tarauni na rubuta wannan wasika ne saboda kira a gareka, a matsayin ka na shugaban al’umma wanda suka amince maka zama shugaban su domin suna da kyakkyawan yakinin cewa zaka musu adalci, kare rayuwar su, tallafa musu da ilimi da ayyukan yi. ‎Ina mai kira da jan hankali dangane da batun sauya fasalin daya daga cikin kasuwannin da suke karkashin kulawar karamar hukumar Tarauni wato kasuwar ‘Yar Kasuwa dake unguwar Gyadi-Gyadi kuma mazabar Gyadi-Gyadi Kudu wacce take mallakin daidaikun mutane ciki harda marayu da…

Read More

A Jihar Kano da ke arewacin Najeriya, aƙalla mutane 10,000 masu cancantar kaɗa ƙuri’a ne suka yi rajistar katin zaɓe a wani babban shiri na kwanaki shida da aka gudanar a jihar. Shirin, wanda aka tsara domin ƙarfafa rajistar masu jefa ƙuri’a, ya samu halartar jama’a da dama, lamarin da masu shirya shi suka ce ya nuna yadda al’umma ke ƙara fahimtar muhimmancin shiga harkokin dimokuraɗiyya. Kano: Indabo Ta Haskaka Ayyukan Gwamnatin Abba Kabir Yusuf Kwamitin da ke kula da shirin ya bayyana cewa sakamakon da aka samu ya zarce hasashen da aka yi tun farko, inda dubban matasa da…

Read More

A Kano, mai bai wa gwamna shawara kan wayar da kai da haɗa kan al’umma, Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo, ta bayyana cewa gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ci gaba da aiwatar da muhimman ayyuka da suka shafi ilimi da lafiya, tare da ƙoƙarin ƙarfafa hulɗa da jama’a. Ta ce daga cikin nasarorin da aka samu akwai gyaran makarantu a sassa daban-daban na jihar, da kuma ɗaukar nauyin karatun ɗalibai zuwa ƙasashen waje domin inganta harkar ilimi. Haka kuma, ta bayyana cewa gwamnatin ta fara ɗaukar nauyin kula da lafiyar mata masu juna biyu a dukkan ƙananan hukumomin jihar, a…

Read More

Mai bai wa Gwamnan Kano shawara kan wayar da kai da haɗa kan al’umma, Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo, ta ƙaddamar da wani shiri na musamman da nufin fito da nasarorin da gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta samu tare da ƙarfafa hulɗa da jama’a a faɗin jihar. An tsara gudanar da taron ne a ranar Litinin, 6 ga Afrilu, 2026, a ɗakin karatu na Murtala Muhammad Library, inda za a gabatar da cikakken bayani mai tushe kan ayyukan da gwamnatin ta aiwatar tun bayan hawanta mulki. INEC Ta Yi Gargadi Kan Yin Rijistar Katin Zaɓe Sau Biyu Indabo ta bayyana…

Read More

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sake gargadin jama’a da su guji yin rijistar katin zaɓe fiye da sau ɗaya, tana mai cewa hakan laifi ne da ke da hukunci mai tsauri a ƙarƙashin dokar zaɓe. Jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar, Hajiya Nahila Bello Dandago, ce ta bayyana hakan yayin wata tattaunawa a gidan rediyon Kano a ranar Asabar. Ta ce duk wanda aka kama da aikata irin wannan laifi na iya fuskantar ɗaurin kurkuku ko tara, ko ma duka biyun. Gwamnatin  Kano Ta Tura Dalibai 550  Domin Taimakawa Wajen Faɗaɗa Rajistar Katin Zaɓe A Fadin…

Read More