A ƙalla mutane 12 ne suka mutu yayin da wasu kusan 38 suka jikkata sakamakon wata gobara da ta tashi bayan fashewar tankar mai a jihar Cross River da ke kudancin Najeriya. Lamarin ya faru ne a ranar Laraba a ƙauyen Ndem, cikin ƙaramar hukumar Ogoja, a lokacin da ake aikin sauya mai daga wata tanka zuwa wata. Rahotanni sun ce tankar ta kife ta fada cikin wani kogi da ke kusa, kafin daga bisani ta kama da wuta, lamarin da ya haddasa gobara mai tsanani. An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje Shaidun…
Author: Kabiru Basiru Fulatan
Majalisar Dattijan Najeriya ta tabbatar da naɗin Dakta Muttaqha Rabe Darma a matsayin ministan gidaje. Hakan ya biyo wasiƙar da shugaba Bola Tinubu ya aike wa Majalisar a Jiya, yana buƙatar ta amince da naɗin. A yayin zaman majalisar, wadda Shugaban majalisar Godswill Akpabio ya jagoranta, ƴan majalisar sun yi wa Dr Darma tambayoyi da dama kan dabarun da zai yi amfani da su wajen magance matsalar ƙarancin gidaje da ƙasar ke fama da ita. Bayan gamsuwa da amsoshin sa, Majalisar ta amince da naɗa shi. A ranar 21 ga watan Afrilun 2026 ne Shugaba Tinubu ya yi wasu sauye-sauye…
Majalisar dattawan Najeriya ta buƙaci gwamnatin ƙasar ta duba yiwuwar dakatar da yaƙin neman zaɓen 2027 a wasu jihohin arewa guda takwas da ke fama da matsalar tsaro. Sanata mai wakiltar Bauchi ta tsakiya Abdul Ningi ne ya gabatar da ƙudurin a zaman majalisar na ranar Alhamis, inda ya ce akwai buƙatar a duba yanayin tashe-tashen hankulan da ake fama da su a ƙasar. Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, Ningi ya ce bai kamata ƴan majalisar su kauda kai daga matsalar tsaron da ke damun wasu sassan ƙasar saboda su suna zaune a Abuja. “Mataki ne da ya zama…
Gwamnatin tarayya ta shigar da ƙarar tuhuma mai ƙunshe da laifuka 13 a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja kan wasu da ake zargi da shirya juyin mulki domin kifar da Shugaba Bola Tinubu kamar yadda jaridar TheCable ta rawaito. Daga cikin waɗanda ake zargin akwai tsohon Manjo Janar, tsohon Kyaftin na rundunar ruwa, wani jami’in ‘yan sanda mai aiki, da wasu mutum uku. Ana zarginsu da aikata laifukan tayar da yaƙi da ƙasa, cin amanar ƙasa da kuma ayyukan ta’addanci. A baya, rundunar tsaro ta tabbatar da cewa akwai shirin juyin mulki a shekarar 2025, inda aka kama…
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa akwai wani sabon shiri na haɗa shi da aikata laifuka domin sake tsare shi. A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar, ya bayyana cewa wannan yunkuri na daga cikin wani tsari na ɓata masa suna da kuma hana shi samun ‘yanci. Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro Sanarwar ta kuma ce El-Rufai na duba yiwuwar ɗaukar matakin shari’a kan jaridar The Nation, bisa wani rahoto da ta wallafa da ke danganta shi da wani hari da aka kai…
Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Olufemi Oluyede ya buƙaci dakarun tsaron ƙasar su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ƴanbindiga a jihohin arewa maso yamma, inda ya nanata cewa dole a tabbatar Najeriya da ƴan Najeriya sun samu tsaro “ta kowane hali.” Janar Oluyede ya bayyana haka a ziyarar da ya kai wa sojojin da suke aiki na musamman na Fansan Yamma a garin Gusau da ke jihar Zamfara. Masarautar Hadejia: Tarihin Shekaru Dari na Turjiyar Hadejia ya Mamayar Yan Mulkin Mallaka, 1906-2026 “Saƙona a fayyace yake: dole dakaru su fita su bi ɓatagari har maɓoyarsu su kawo ƙarshensu. Dole mu…
Masarautar Hadejia ta sanar da shirinta na gudanar da babban taron tunawa da cika shekaru 120 da yaƙin da al’ummar Hadejia suka yi da Turawan mulkin mallaka a shekarar 1906, wani lamari da ake kallonsa a matsayin muhimmin ginshiƙi a tarihin yankin. Taron zai gudana ne karkashin jagorancin Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje Haruna, CON, a madadin daukacin al’ummar masarautar. BH Startup Da Faster Capital Sun Haɗa Kai Domin ƙarfafa Harkar Sarrafa Shinkafa A Arewacin Najeriya Da yake jawabi ga manema labarai, Galadiman Hadejia, Alhaji Usman Abdul’aziz, ya bayyana cewa wannan taro ba wai na nishadi…
Al’ummar ‘yan jarida a jihar Kano na jimamin rasuwar fitaccen ɗan jarida da ya shahara wajen rahotannin kotu da laifuka, Balarabe Nazeephy, wanda aka fi sani da “Wakilin Kotu da ’Yan Sanda.” Rahotanni sun ce marigayin ya rasu ne bayan ya shafe sama da shekaru talatin yana aikin jarida, inda ya yi fice wajen rahoto kan harkokin shari’a da tsaro cikin ƙwarewa da jajircewa. Nazeephy ya samu karɓuwa a tsakanin abokan aikinsa, lauyoyi da jami’an tsaro, sakamakon yadda yake gabatar da rahotanni cikin inganci da gaskiya. Wani ɗan jarida, Abbas Ibrahim, ya bayyana cewa marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen…
A ranar Lahadi, 12 ga watan Afrilu, 2026, an gudanar da bikin aure biyu a Masallacin Anas Bin Malik da ke unguwar Sheka Achilafiya, inda iyalai da abokai suka hallara domin shaida wannan muhimmin biki. Bikin ya hada auren Aliyu Abdullahi Idris, wanda aka fi sani da “Butter”, da Hauwa’u U. Abdullahi Alhassan. Haka kuma a wannan rana aka daura auren Khadija Abdullahi Idris da Usman Ismail. Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa Mahaifin ango da amarya, Abdullahi Idris, ya bayyana godiyarsa ga Allah bisa nasarar gudanar da bikin lafiya, tare da yaba…
Wani mummunan lamari ya auku a kan iyakar Jihar Borno da Jihar Yobe, inda rahotanni ke cewa wani hari daga sama da sojoji suka kai ya fada kan wata kasuwa ta al’umma, lamarin da ake fargabar ya hallaka fiye da mutane 50. Bisa ga bayanan da ke fitowa a hankali, an ce harin ya faru ne yayin wani samame da ake kai wa ‘yan tada kayar baya a yankin Arewa maso Gabas. Sai dai abin takaici, fararen hula sun tsinci kansu a cikin harin, wanda ya jawo asarar rayuka da raunuka masu yawa INEC ta ɗage aikin sabunta bayanan rajistar…