Author: Kabiru Basiru Fulatan

DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM  Hukumar yaƙi da safarar mutane a Najeriya NAPTIP ta kuɓutar da mutum 15 har da baƙi bayan da ta bankaɗo wata ƙungiyar masu safarar mutane da ake zargi tana aiki a matsayin kamfanin tallata kayayyaki ta intanet a jihar Nasarawa. NAPTIP ta kuɓutar da mutanen ne bayan samamen da jami’anta suka kai ƙananan hukumomin Karu da Keffi sakamakon sahihan bayanan da suka samu a kan kamfanin. Najeriya Za Ta Kashe Dala Biliyan 11.6 Wajen Biyan Kudin Ruwan Basussuka A 2026 — Shugaba Tinubu NAPTIP ta sanar da haka ne cikin sanarwar da ta wallafa a…

Read More

DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya za ta kashe kimanin dala biliyan 11.6 wajen biyan kuɗaɗen ruwa da sauran basussukan da ake bin Najeriya a shekarar 2026. Tinubu ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin jawabi a taron Africa Forward Summit da aka gudanar a cibiyar taruka ta Kenyatta International Convention Centre da ke birnin Nairobi. Rikicin ACF: Lokaci Ya Yi Na Rushe Tsohon Tsari Da Yin Garambawul —Abbas Ibrahim  A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar, shugaban ya ce kuɗin da za a kashe…

Read More

Rikicin da ke girgiza kungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ya kamata ya zama lokaci na zurfin tunani ga shugabannin Arewa maimakon ci gaba da fafutukar neman iko. An kafa ACF ne domin hada kan Arewacin Najeriya, kare muradunta, inganta zaman lafiya, da bayar da jagoranci kan al’amuran da suka shafi yankin. Idan rikice rikicen cikin gida suka rikide zuwa zarge zargen cin hanci, killace ofisoshi da ‘yan sanda, da rudanin kundin tsarin mulki, to martabar Arewa gaba daya ce ke tabarbarewa a idanun kasa baki daya. Abin da ya fara a matsayin sabani tsakanin Kwamitin zartarwa a matakin kasa da…

Read More

Shekaru 78 da suka gabata, a shekarar 1948, ƙasar Costa Rica ta ɗauki wani mataki da har yanzu ƙasashe da dama ke kallonsa a matsayin abin mamaki, inda ta rusa rundunar sojinta gaba ɗaya ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban ƙasar, José Figueres Ferrer. Matakin bai samo asali daga yalwar zaman lafiya ko wadata ba, sai dai daga darasin siyasa mai ɗaci da ƙasar ta koya bayan wata gajeriyar amma mummunar arangama ta yaƙin basasa. A lokacin, jama’a da dama sun gaji da yadda rundunonin soji ke zama kayan aikin juyin mulki da tsoratarwa a ƙasashen Latin Amurka. Shugabannin Costa Rica sun…

Read More

Hadakar Malamai da Kungiyoyin Musulunci a Jihar Kano sun yi kira ga ‘yan siyasa da magoya bayansu da su guji kalaman tunzura jama’a tare da gudanar da harkokin siyasa cikin lumana domin kare zaman lafiya a jihar. A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda ake samun zafafan kalamai da wasu dabi’u da ka iya haddasa tashin hankali a tsakanin masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa. Ƙalubalen Da Masu Ƙananan Sana’o’i Ke Fuskanta Saboda Ƙarancin Wutar Lantarki A Kano  ‎ ‎ Kungiyar ta ce siyasa bai kamata ta zama hanyar haifar da rikici ko…

Read More

Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh. ‎ ‎Da farko, ina miƙa godiya ta musamman ga Allah Maɗaukakin Sarki, wanda Ya ba mu damar kasancewa tare a wannan muhimmin taro na Ranar Ma’aikata ta Duniya ta shekarar 2026. ‎Ina kuma taya dukkan ma’aikata a Jihar Kano, Najeriya da duniya baki ɗaya murna bisa wannan rana mai muhimmanci, wadda ke tunatar da mu irin rawar da ma’aikata ke takawa wajen gina al’umma mai dorewa. ‎ ‎Hakika, ma’aikata su ne ginshiƙin ci gaban kowace ƙasa. Ba za a iya samun cigaba mai ma’ana ba tare da jajircewarsu, sadaukarwarsu, da ƙwazon aikinsu ba. Saboda…

Read More

Masu ƙananan sana’o’i a Jihar Kano na ci gaba da kokawa kan yadda ƙarancin wutar lantarki ke janyo musu asara tare da kawo cikas ga ci gaban harkokinsu a daidai lokacin da ake fama da tsadar rayuwa a faɗin ƙasar. ‎Binciken Jaridar Inda Ranka ya nuna cewa yawan katsewar wutar lantarki ya tilasta wa masu sana’o’i, musamman masu ɗinki, masu walda da masu sana’ar sanyi, komawa amfani da janareta da sola domin ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum. ‎Aman Wuta: Sama da Mutane 5,000 Sun Tsere Daga Gidajensu a Philippines ‎Sai dai, hauhawar farashin man fetur…

Read More

‎Tsohon ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Bichi, Hon. Mahmoud Baba Bichi, ya ayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Sanatan Kano Ta Arewa a zaɓen 2027 karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC). ‎Bichi ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyara sakatariyar jam’iyyar APC ta Jihar Kano, inda ya ce ya zo ne domin sanar da shugabannin jam’iyyar kudirinsa na neman kujerar majalisar dattawa. ‎Samar da Aminci, Shi Ne Farko — Dole a Kawar Da Siyasar Dauka Makamai Daga Fagen Siyasar Kano ‎Ya bayyana cewa tuni ya sayi fom ɗin tsayawa takara a hedikwatar APC ta ƙasa da ke…

Read More

‎Daga Comrade Abbas Ibrahim ‎Yayin da Jihar Kano ke tunkarar wani muhimmin mataki a harkokin siyasa na Babban Zaɓen 2027, bukatar daukar matakan da suka dace domin kare rayuka, dukiyoyi da martabar dimokuradiyya na kara zama wajibi fiye da kowane lokaci. Haramta daukar makamai a wuraren tarukan siyasa ba zabin son rai ba ne, wajibi ne. ‎Rikicin da ya faru a ranar Litinin, 27 ga Afrilu, 2026, a kusa da kasuwar Farm Centre dake Kano, ya sake fito da yadda tarukan siyasa ke iya rikidewa zuwa tashin hankali idan aka bar magoya baya ba tare da kulawa da takunkumi ba.…

Read More

DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM  Fiye da mutane 5,000 ne suka tsere daga gidajensu a ƙasar Philippines bayan da dutsen mai aman wuta Dutsen Mayon ya fara fitar da toka mai yawa, lamarin da ya jefa al’umma cikin fargaba. Rahotanni sun bayyana cewa dutsen da ke yankin Bicol ya fitar da gagarumar toka da ta mamaye sararin samaniya, lamarin da ya tilasta wa mazauna yankunan da ke kusa da shi barin gidajensu domin tsira da rayukansu. Yadda za a Fara Jigilar Maniyatta Aikin Hajji a Ƙasar nan. A cewar hukumomi, mutanen da abin ya shafa sun samu mafaka a sansanonin wucin…

Read More