Gwamnatin Jihar Kano ta tura dalibai 550 daga cibiyoyin ilimi tara domin taimakawa wajen faɗaɗa rajistar rajistar masu zaɓe CVR, a wani yunƙuri na ƙara ƙarfafa shiga harkokin dimokuraɗiyya a faɗin jihar. Shugaban Kwamitin Ƙarfafa Rajistar Masu Zaɓe na Jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da shirin a filin wasanni na Kofar Mata, inda ake gudanar da babban aikin rajistar masu zaɓe. Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Abbas Ibrahim, Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai, ya fitar a madadin Kwamitin Ƙarfafa Rajistar Masu Zaɓe na Jihar Kano. A cewar Waiya, an horas da…
Author: Kabiru Basiru Fulatan
A Jihar Kano, an ƙaddamar da wani shiri na kwanaki shida na rajistar Katin zaɓe, a wani yunƙuri na ƙara yawan masu katin zaɓe da kuma ƙarfafa shiga harkokin dimokuraɗiyya. Shugaban Kwamitin Ƙarfafa Rajistar Masu Katin Zaɓe na jihar, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya jagoranci ƙaddamar da shirin a ranar Laraba a cibiyar wasanni da ke Kofar Mata. A cewarsa, an tanadi rumfunan rajista guda 20 domin sauƙaƙa wa jama’a yin rajista cikin gaggawa da kuma rage cunkoso. Waiya ya bayyana gamsuwarsa kan yadda jama’a suka fito domin yin rajistar, yana mai cewa hakan na nuna fahimtar al’umma kan…
A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da shirin kula da lafiya na Hukumar KACHMA, ke fuskantar matsaloli wajen samun magunguna, duk da kasancewarsu cikin tsarin. Shirin kula da lafiya na Hukumar KACHMA tsari ne na taimakekeniya domin tallafawa masu rauni, musamman mata da tsofaffi, domin samun kulawa ta musamman. Bankin CBN Ya Fitar Da Sunayen Bankuna 33 Da Suka Cika Ƙa’idar Ƙara Jarinsu Rahotanni sun nuna cewa, matsalar gudanar da shirin ta fi shafar mata da tsofaffi marasa lafiya. Wakilanmu sun lura da cewa, matsalar ta fi k’amari a asibitin K’wararru na…
Babban Bankin Najeriya CBN ya fitar da sunayen bankuna 33 da ya amince cewa jarinsu ya kai su ci gaba da gudanar da hada-hada a cikin ƙasar, a wani yunƙuri na kare dukiyoyin abokan hulɗarsu. Cikin wata sanarwa da CBN ya fitar a jiya Laraba, ya ce shirin wanda aka soma tun watan Maris na shekarar 2024, an kammala shi a yanzu bayan shafe watanni 24 ana yinsa, domin ƙarfafa tsarin hada-hadar kuɗi tsakanin bankuna da abokan hulɗarsu a Najeriya. Babban bankin ya ce bankunan 33 da aka amince dasu sun samar da jari na Naira tiriliyan 4 da biliyan…
Tsohon mataimakin gwamnan Kano kuma tsohon ɗan takarar gwamnan jihar a jam’iyyar APC ya karɓi katin jam’iyyar ADC a hukumance, a ranar Litinin. A ranar Lahadi ne ya sanar da ficewa daga jam’iyyar APC, tare da jadadda mubaya’arsa ga tsarin Kwankwasiyya. Gawuna Ya Fice Daga Jam’iyyar APC Bayanai na cewa komawar tasa na da alaƙa da rashin yadda ake zargin mayar da shi saniyar ware a jam’iyyar APC. Tundai bayan da kotun koli ta Najeriya ta tabbatar wa da Abba Kabir Yusuf kujerar gwamnan Kano, wasu magoya bayan Nasiru Gawuna suka yi ta sa ran shugaba Tinubu zai bai wa…
Tsohon mataimakin gwamnan Jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC). A cikin wata takardar murabus mai ɗauke da kwanan watan 29 ga Maris, 2026, wadda ya aikewa shugaban jam’iyyar a mazabarsa ta Gawuna da ke karamar hukumar Nassarawa, Gawuna ya ce matakin da ya dauka na barin jam’iyyar na son rai ne kuma na kashin kansa. Gawuna ya sauka daga shugabancin kwamitin Gudanarwa na Bankin Lamuni na Tarayya. Ya bayyana a cikin takardar cewa: “Ina sanar da ku a hukumance cewa na fice daga jam’iyyar APC daga ranar 29 ga Maris, 2026.”…
Nasiru Gawuna, jigo a jam’iyyar APC a Kano kuma Shugaban hukumar FMBN, ya ajiye mukaminsa. Gawuna ya ce murabus ɗin nasa ya fara aiki nan take, kuma ya yi dai-dai da umarnin shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na cewa duk masu riƙe da mukaman siyasa su sauka gabanin wasu harkokin siyasa. Shugaban NUJ Ya Yaba Da Aikin Kano Correspondents’ Chapel, Ya Kira ‘Yan Jarida Su Kara Hadin Kai Ya godewa shugaban Ƙasa bisa damar da aka ba shi na yin aiki, inda ya bayyana cewa hakan wata babbar dama ce. Rahotanni sun kuma nuna cewa Gawuna na shirin sauya sheƙa…
Shugaban ƙasa na Alhassan Yahya, ya yaba wa shugabannin ƙungiyar Kano Correspondents’ Chapel, NUJ saboda kafa ginshikin da ke karfafa kauna, hadin kai, da ci gaba a tsakanin ‘yan jarida a jihar Kano. Kwamared Yahya ya bayyana wannan ne a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Kano a ranar Lahadi, a yayin taron walimar cin abinci da godiya ga Allah da ‘yan jaridar suka shirya bayan kammala Ibadar Azumin watan Ramadhana da kuma bukin Sallah. Sheikh Pantami Ya Roƙi El-Rufai, Ribadu Da Uba Sani Su Sulhunta A Jana’izar Mahaifiyarsa A jawabin sa, Shugaban NUJ ya bukaci mambobin kungiyar su ci gaba da…
Sheikh Dr. Isa Pantami ya buƙaci Malam Nasir El-Rufai da abokan siyasarsa su ajiye saɓanin da ke tsakaninsu, ya yi wannan kiran ne a makabarta yayin binne mahaifiyar El-Rufai, Hajiya Umma, a Abuja. Pantami ya yi wannan kira ne a huɗubarsa a maƙabartar Gudu ranar Lahadi. Ya roƙi shugabanni su fifita haɗin kai tare da tunawa da alherin da suka yi wa juna. Ya jaddada cewa rayuwa mai wucewa ce kuma dole kowa ya bar duniya wata rana. Ya ƙara da cewa nasara na zuwa ne ta bin hanyar Allah ba dabarun siyasa ba. A wurin jana’izar, manyan ‘yan siyasa…
Tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP nan take. Kwankwaso, wanda ya kasance jagoran jam’iyyar na kasa kuma dan takararta a zaben shugaban kasa na 2023, ya bayyana cewa ya dauki matakin ne bayan nazari kan yanayin siyasar kasar, domin samun wata sabuwar hanya da za ta ba shi damar kawo sauyi mai ma’ana. WAEC: Ɗalibai Sama da 10,000 Sun Rubuta Jarabawa, Kashi 32% Sun Samu Credits Biyar Ya gode wa shugabannin jam’iyyar, ciki har da shugaban jam’iyyar, Ajuji Ahmed, da sauran mambobin kwamitin gudanarwa na kasa, bisa goyon bayan da suka…