Author: Kabiru Basiru Fulatan

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya sauke kwamishinoninsa guda shida daga kan muƙamansu, a wani ƙwarya-ƙwaryar garambawul da ya yi domin ƙara inganta gwamnatinsa. Daga Zainab Kamal Ibrahim  Sakataren Gwamnatin Jihar, Labaran Magaji, shi ya sanar da hakan yayin wani ƙarin haske ga ƴan jaridu bayan tashi daga zaman majalisar zartarwar jihar a ranar Talata, Magaji ya ce kwamishinonin da lamarin ya shafa sun haɗar dana Ma’aikatun Ayyuka, Harkokin Mata, Yaɗa Labarai, Ƙasa, Kimiyya da Fasaha, da kuma Ma’aikatar Tsaro. Uba Ya Rasa Ransa Yayin Ƙoƙarin Ceto ‘Yarsa Da Ta Faɗa Rijiya A Kano Ya kuma bayyana cewa…

Read More

Wani mutum mai suna Abubakar Abdullahi, mai shekaru 45, da ‘yarsa Fiddausi, mai shekaru 15, sun rasu bayan sun faɗa cikin wata rijiya a garin ‘Yancibi da ke Ƙaramar Hukumar Tsanyawa a Jihar Kano. Daga Zainab Kamal Ibrahim Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata, lokacin da Fiddausi ta faɗa cikin rijiyar. Mahaifinta, Abubakar Abdullahi, ya shiga rijiyar ne domin ceto ta, amma abin takaici shi ma ya makale a ciki. Gwamna Abba Ya Kaddamar Da Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sa Hannu Kan Dokar Hana Daba A Kano Kakakin Hukumar Kashe Gobara…

Read More

Gammon Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da Kwamitin Haɗin Gwiwa na Hukumomi kan Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, tare da sanya hannu kan Dokar Zartarwa da za ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da daba da sauran ayyukan ta’addanci a jihar. Daga Zainab Kamal Ibrahim  Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba. A cewar gwamnan, shaye-shayen miyagun ƙwayoyi na daga cikin manyan matsalolin da ke barazana ga makomar matasan Kano, saboda yana haddasa aikata laifuka, lalata iyalai, raunana tattalin…

Read More

Hukumar Kula da Albarkatun Ruwa ta Ƙasa (NIHSA) ta yi gargaɗin cewa jihohi 17 na Najeriya na fuskantar barazanar ambaliyar ruwa tsakanin ranar 21 zuwa 27 ga watan Yulin 2026. Daga Zainab Kamal Ibrahim Hukumar ta ce hakan na zuwa ne bayan da wasu manyan koguna da madatsun ruwa suka tumbatsa, lamarin da ka iya haddasa ambaliya a yankuna da dama. Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Shirin Bashin Laptop Ga Matasa Babban Daraktan NIHSA, Umar Ibrahim Mohammed, ya ce binciken da hukumar ta gudanar ya nuna cewa Kogin Karam da Madatsar Waya da kuma Kogin Amber sun cika…

Read More

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani sabon shiri na bai wa matasa damar samun kwamfutocin tafi-da-gidanka (Laptop) ta hanyar bashi mai sauƙin biya, domin ƙara musu damar cin gajiyar tattalin arzikin zamani. Daga Zainab Kamal Ibrahim  Shirin, wanda Hukumar Bayar da Lamuni ta Ƙasa (CREDICORP) ta ƙaddamar tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Sadarwa, Ƙirƙire-ƙirƙire da Tattalin Arzikin Zamani ta Tarayya, an sanya masa suna Credit for Laptops, Internet, Connectivity and Knowledge Digital Devices (C.L.I.C.K.D.). A matakin farko, shirin zai samar da laptop 1,000 da aka haɗa a Najeriya ga waɗanda suka cancanta daga cikin mahalarta shirin horas da…

Read More

Ana zargin wani mutum da yanka matarsa, Fatima Muhammad, da kuma ɗansu Masaud Nazir da wuka a unguwar Samaigu da ke Jihar Kano. Daga Zainab Kamal Ibrahim  Rahotanni sun ce mutumin ya caka wa matarsa wuka a gefen cikinta, yayin da ɗansu ya samu raunuka a hannunsa da kuma kansa. Wata maƙwabciyar iyalan ta tabbatar wa wakilinmu cewa lamarin ya faru, sai dai ta ce ba ta da cikakken bayani kan yadda abin ya faru ko kuma abin da ya haddasa rikicin. Kwamitin Ƙwadago Ya Buƙaci Jama’a Su Gaggauta Yin Rijistar Katin Zaɓe Kafin Wa’adi Ya Cika Har zuwa lokacin…

Read More

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya bayyana cewa buɗe asusun Hukumar PFIPC ya biyo bayan umarnin da Ofishin Akanta Janar na Tarayya ya bayar, ba tare da bankin ya yi hakan da kansa ba. Daga Zainab Kamal Ibrahim  Wannan bayani ya fito ne ta bakin wani babban darakta a CBN, Hamisu Abdullahi, yayin da yake wakiltar Gwamnan Babban Bankin a gaban Kwamitin Majalisar Wakilai da ke binciken sahihancin kafuwar hukumar PFIPC. A cewarsa, shugaban hukumar ya gabatar da takardun da suka nuna cewa Ofishin Akanta Janar na Tarayya ne ya bayar da umarnin buɗe asusun hukumar a ranar 30…

Read More

Likitan tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, Dakta Bello Abubakar, na fuskantar bincike daga hukumomin da ke kula da harkokin likitanci a Najeriya, bayan zargin bayar da rahoton jinya na bogi. Daga Zainab Kamal Ibrahim  Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya biyo bayan gurfanar da likitan a gaban kotu da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta yi, bisa zargin gabatar da rahoton jinya da ake cewa ba sahihi ba domin tallafa wa buƙatar belin tsohon gwamnan a wata shari’a. A cewar ICPC, ana tuhumar Dakta Bello Abubakar da laifuka huɗu, ciki har da zargin bai…

Read More

DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM  Mutane biyu sun rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a yammacin ranar Litinin a yankin Olorunsogo da ke unguwar Leme, a Karamar Hukumar Abeokuta ta Kudu, Jihar Ogun.‎ ‎Rahotanni sun ce hatsarin ya afku da misalin karfe 5:45 na yamma, inda wata mota kirar Lexus ta yi karo da wani babur kirar TVS. ‎ ‎Shaidun gani da ido sun bayyana cewa motar Lexus na tafiya cikin tsananin gudu lokacin da ta bugi babur din. Direban babur ya mutu nan take bayan ya samu mummunan rauni a kansa. ‎FIFA Ta Fitar Da Sabon…

Read More

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (ICPC) ta gayyaci Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, domin yi masa tambayoyi kan rawar da ake zargin ya taka a batun wata hukuma da ta janyo ce-ce-ku-ce bayan an bayyana cewa ba ta da sahalewar gwamnati Daga Zainab Kamal Ibrahim  Lauyan Gbajabiamila, Jiti Ogunye, ya tabbatar da cewa ya bayyana a hedikwatar ICPC a ranar Litinin, inda jami’an hukumar suka masa tambayoyi kan zarge-zargen da suka shafi PFIPC. Sai dai ya ce ya amsa dukkan tambayoyin da aka yi masa tare da ba da haɗin kai ga masu bincike.…

Read More