Zainab Kamal Ibrahim A ranar Lahadin nan ne ake sa ran jirgin farko na maniyyata aikin Hajjin bana ta shekarar (2026) na ƙasar zai tashi zuwa Saudiyya arabiyya don gudanar da aikin Hajjin bana. Hukumar alhazan ta ƙasar nan NAHCON, ta ce an kammala dukkan shirye-shirye da Ake gudanarwa don gudanar da jigilar maniyyata cikin nasara. Hukumar ta ja hankalin maniyyatan ƙasar nan kan abubuwan da ya kamata su kiyaye, domin kauce wa matsala a ƙasar ta Saudiyya. Tin da fari, mataimakiyar Darakta Fatima Sanda Usara,ta ce a sashen yada labaran hukumar, ta ce kawo yanzu hukumar na ci gaba…
Author: Kabiru Basiru Fulatan
Sakataren Gwamnatin Jihar Kano (SSG), Alhaji Umar Faruk Ibrahim, ya ce bincike ya tabbatar da cewa kamfanonin bada bashi ne suka cire sama da Naira biliyan 1.5 daga albashin ma’aikatan jihar, ba tare da hannun jami’an gwamnati ba. Kano City Guide SSG ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin bikin ranar ma’aikata ta duniya da ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC suka shirya a Fadar Gwamnatin Kano. Amurka Ta Sanar Da Shirin Janye Sojojinta 5,000 Daga Jamus. Ya ce binciken da wani kwamitin gwamnati ya gudanar tare da haɗin gwiwar wani kamfanin bincike mai zaman kansa ya gano cewa…
DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM Ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta sanar da cewa za ta janye dakarun soji kimanin 5,000 daga Jamus. Amurka ta yi barazanar janye sojojinta da ke ƙasashen Italiya da Spain. Wannan matakin ya zo ne a daidai lokacin da aka samu rashin jituwa tsakanin Shugaban kasan Amurika Donald Trump da sabon Shugaban Gwamnatin Jamus, Friedrich Merz. Donald Trump ya bayyana hakane bayan da Merz ya soki dabarun Amurka a yaƙin da take yi da Iran, inda ya bayyana cewa Iran ta kunyata Amurka a tattaunawar neman zaman lafiya. A kasar. Sai daii Shugaban kasar Amurika Trump…
DAGA ZAINAB KAMAL IBRAHIM Matatar man Dangote dake Najeriya ta sanar da dawo da wasu daga cikin ma’aikatanta na injiniyoyin da ta ladabtar da su wajen tura su aiki a wasu ma’aikatu, sakamakon wani laifi da suka yi a baya. Sanarwar da kamfanin dillancin labarai ya fitar ya ce dawo da waɗannan ma’aikata ya biyo bayan afuwar da akai musu bayan ɗaukar matakan ladabtarwa ta cikin gida. Kotun ƙoli ta kori ƙarar PDP ɓangaren Tanimu Turaki Jaridar The Cable ta wallafa cewaa ƙasar ta ɗauki matakin dawo da ma’aikata bakin aikin su, ya biyo bayan sanya hannu da kuma…
Kotun ƙolin Najeriya ta kori ƙarar da shugabancin PDP tsagin Tanimu Turaki ya shigar, inda yake ƙalubalantar matakin rushe taron zaɓen shugabanninsu da aka yi a Ibadan. Yayin da yake sanar da matsayar alƙalan, mai shari’a Stepehen Adah ya bayyana cewa taron da suka gudanar a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamban 2025 a Ibadan rashin ɗa’a ne ga hukuncin babbar kotun tarayya da mai shari’a James Omotosho ya yanke inda ya dakatar da su daga gudanar da babban taron jam’iyyar. Shugaba Tinubu ya aike da sunan Joseph Tegbe ga mjalisa don tantance shi a matsayin Ministan Lantarki Kotun…
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunan Mista Joseph Olasunkanmi Tegbe zuwa Majalisar Dattawa domin tabbatar da shi a matsayin sabon Ministan Lantarki na ƙasar nan. Wannan sanarwa tana ƙunshe ne a cikin wata takarda da Mai Magana da Yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu, 2026. HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim Naɗin na Tegbe ya biyo bayan murabus ɗin da tsohon Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu ya yi, domin shiga takarar zaɓe. Waye Joseph Tegbe? Tegbe, wanda ɗan asalin Jihar…
Harin da wasu da ake zargin ’yan daba masu alaƙa da siyasa suka kai Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Cente da ke Kano ya janyo hankalin jama’a, inda ake ganin lamarin wata babbar barazana ce ga zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a jihar, musamman yayin da ake tunkarar zaɓen 2027. Lamarin ya faru ne a ranar Litinin, 27 ga Afrilu, 2026, inda aka ga yadda wasu suka mamaye kasuwar, suka yi sace-sace, tare da lalata dukiyoyi ciki har da motoci da babura. Haka kuma, mutane da dama sun samu raunuka a yayin harin. Kano: Gwamnati Ta Fara…
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da kammala shirye-shirye domin gudanar da bikin Ranar Ma’aikata ta shekarar 2026 cikin tsari mai kyau. Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin jihar, Hajiya Bilkisu Shehu Maimota, ce ta bayyana hakan a yayin wani taron shiri da ya haɗa da Kwamishinan Yaɗa Labarai, wakilan ƙungiyoyin ƙwadago da sauran masu ruwa da tsaki. Dangote na shirin gina katafariyar matatar mai a gabashin Afirka Ta ce gwamnati na da niyyar shirya biki mai armashi da zai nuna muhimmancin rawar da ma’aikata ke takawa wajen ci gaban jihar. A cewarta, kyakkyawar alaka tsakanin gwamnati da ƙungiyoyin ƙwadago na taimakawa wajen inganta…
Hamshaƙin attajirin nahiyar Afirka, Aliko Dangote ya bayyana shirin gina katafariyar matatar man fetur da za ta iya tace ganga 650,000 a kowace rana a gabashin Afirka. Yayin da yake jawabi a wani babban taron masu ruwa da tsaki kan masana’antun Afirka, da ke gudana a birnin Nairobin Kenya, Dangote ya ce shirin wani mataki ne na bunƙasa masana’antu a nahiyar. Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda Taron – wanda manyan shugabannin Afirka da masu zuba jari da masu ruwa da tsaki kan harkar masana’antu suka halarta – an shirya shi ne…
Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka a Jihar Kano na da alaƙa da shan miyagun ƙwayoyi da fataucinsu, lamarin da ya nuna yadda matsalar ke da nasaba da rikice-rikicen daba da a yankin. Rahoton sirri da aka samu ya nuna cewa shan miyagun ƙwayoyi ya zama babban abin da ke ƙarfafa ƙungiyoyin daba, waɗanda ke shiga rikice-rikicen tashin hankali, hare-haren makamai da faɗace-faɗacen titi a sassan jihar. Rahotan, wanda rundunar ‘yansandan Jihar Kano ta tattara ƙarƙashin jagorancin kwamishinan ‘yansanda Ibrahim Adamu Bakori, ta nuna cewa an kama mutane 3,081 da ake…