Author: Kabiru Basiru Fulatan

A sanarwar da mukaddashin shugaban hulɗa da jama’a na hukumar, Moyosola F. Adesina ya fitar daga hedikwatar WAEC da ke Yaba, ya ce an gudanar da jarabawar ne a cibiyoyi 166 a faɗin Najeriya daga 28 ga Janairu zuwa 14 ga Fabrairu 2026. Jimillar ɗalibai 10,480 ne suka rubuta jarabawar, daga ciki dalibai 3,429 kashi 32.72% sun samu credit a akalla darussa biyar ciki har da Turanci da Lissafi. An rantsar da Ali Musa Hardwoker a matsayin halartaccen shugaban karamar hukumar Kumbotso a Kano Wannan ya nuna ƙaruwa da kashi 5.76% idan aka kwatanta da sakamakon shekarar 2025 wanda ya…

Read More

Hukumar Zabe ta jihar Kano KANSIEC ta rantsar da Honarabul. Ali Musa Ɗanmaliki, (Hardwoker) a matsayin halartaccen shugaban karamar hukumar Kumbotso a Kano. Hukumar ta rantsar da Hardwoker, ne a yau Talata, bayan sauke Abdullahi Ghali Basaf daga shugaban karamar hukumar Kumbotso, yayin da aka maye gurbin sa da Ali Musa. Matatar Ɗangote ta fitar da tan 456,000 na man fetur zuwa wasu ƙasashen Afrika Bayan hukuncin babbar kotun jihar Kano na sauke Ghali Abdullahi Basaf daga shugabancin ƙaramar hukumar Kumbotso, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano ta mika shedar lashe zaɓe ga Hon. Ali Musa Hardworker. Shugaban…

Read More

Mamatar mai ta Ɗangote ta sanar da fara fitar da tataccen man fetur zuwa wasu ƙasashen Afrika, matakin da ke zuwa bayan da tayi iƙirarin wadata kasuwar cikin gida a Najeriya, duk da tsadar da yake yi a gidajen mai. Bayanai sun ce an fitar da manyan jiragen dakon man fetur guda 12 ɗauke da tan dubu 450 zuwa wasu ƙasashen Afrika biyar waɗanda rikicin gabas ta tsakiya ya fi yiwa fannin makamashinsu illa. Jami’an Hisbah Sun Kama Matasa Kusan 300 Da Suka Yi Askin Banza Da Kuma Kitso A Kano  Kafafen yaɗa labarai na cikin gida a Najeriya sun…

Read More

Hukumar Hisbah a jihar Kano ta kama matasa sama da 250 kan yin askin banza ko kuma kitse gashinsu. Mataimakin babban kwamandan hukumar, Mujahid Aminudden ne ya bayyana haka a bayanin da ya fitar game da ayyukan rundunar a bikin karamar Sallah. Ya ce daga cikin matasan akwai matuka Adaidaita Sahu da ke daukan mata a gefen baburansu. Gabanin bikin Sallar dai, hukumar ta fitar da sanarwar gargadi musamman ga matasa, kan kiyaye ayyukan da suka saba da tanadin addini da al’adun mutanen Kano.

Read More

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya al’ummar Musulmi murnar bikin ƙaramar Sallah, tare da kira gare su da su ƙara ƙaimi wajen nuna kishin ƙasa da kuma ƙarfafa haɗin kai a tsakanin al’umma. ‎A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis, shugaban ya jaddada muhimmancin ci gaba da riƙe darussan da aka koya a watan Ramadan. ‎Ya ce darussa irin su tsoron Allah, haƙuri, tausayi da sadaukarwa na da muhimmanci wajen gina al’umma mai zaman lafiya, yana mai kira ga Musulmi da su ci gaba da amfani…

Read More

‎ Jam’iyyar Labour Party ta bayyana cewa za ta gudanar da Zaben fitar Gwani na  shugaban ƙasa na cikin gida ranar 23 ga Mayu, 2026, a matsayin shiri na tunkarar babban zaɓen 2027. ‎A lokaci guda, jam’iyyar ta dakatar da membobi 25 saboda zargin aikata abubuwa marasa kyau da suka saba wa ka’idojin jam’iyya. ‎Hukuncin ya fito ne daga taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) da aka gudanar a ranar Talata, inda Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanya ido. ‎Jam’iyyar ta ce za a miƙa jerin sunayen mambobi ga INEC ranar 15 ga Afrilu, 2026, yayin…

Read More

‎Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka CAF ta kwace kofin zakarun nahiyar Afirka na 2025 daga ƙasar Senegal, tare da bai wa Morocco nasarar zama zakarun gasar. ‎Sanarwar da CAF ta fitar ta ce kwamitin sauraron ƙorafi na hukumar ya yanke hukuncin cewa tawagar Senegal ta karya dokokin gasar, bayan da wasu daga cikin ’yan wasanta suka fice daga filin wasa a yayin wasan ƙarshe domin nuna rashin amincewa da hukuncin alƙali.‎ ‎Hukumar ta ƙara da cewa an ayyana Senegal da laifin watsi da wasa, wanda ya sa aka sauya sakamakon wasan daga 1-0 da Senegal ta samu zuwa 3-0 a…

Read More

Kungiyoyin goyon bayan jam’iyyar APC guda dubu ɗaya da ɗari biyar (1,500) da aka yi wa rajista sun amince da marawa shirin Renewed Hope Network (TRN) na Sanata Abdul’aziz Yari a matsayin wata kafa ta musamman da aka ƙirƙira domin wayar da kan jama’a domin tabbatar da sake zaɓen Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu karo na biyu a shekarar 2027. Wata sanarwa da Mataimakin Darakta Janar na gamayyar kungiyoyin, Dakta AK Peters, ya sanya wa hannu a Abuja, ta bayyana cewa bayan wani muhimmin taro, TRN ƙarƙashin jagorancin gogaggen mai wayar da kan jama’a na APC kuma tsohon Babban Mataimaki…

Read More

Gwamnatin Jihar Kano ta musanta rahotannin da ke cewa Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, zai jagoranci hawan Sallah mai zuwa a jihar. A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida  Ibrahim Abdullahi Waiya ya fitar, sanarwar ta ce rahoton da ke yawo a wasu kafafen yaɗa labarai da kuma shafukan sada zumunta ba shi da tushe. Jami’an tsaro Sun Dakile Yunƙurin Sace Ɗalibai A Kwalejin ’Yan Mata A Bauchi Ta bayyana cewa har yanzu ba a yanke wani hukunci a hukumance dangane da batun jagorancin hawan Sallah ba. Gwamnatin ta ƙara da cewa batun…

Read More

Jami’an tsaro a Jihar Bauchi sun dakile wani yunƙurin sace ɗalibai a Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnati (Government Girls’ College) da ke jihar, bayan wasu da ba a san ko su wanene ba sun yi ƙoƙarin shiga harabar makarantar. Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe huɗu na asubahin ranar Lahadi 15 ga watan Maris, lokacin da wasu mutane suka yi yunƙurin tsallaka katangar makarantar ta wani ɓangare da ke kusa da gidajen ma’aikata. Hatsarin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna ya jikkata mutane da dama Jaridar TheCable, wadda ta ruwaito rahoton daga majiyar tsaro Zagazola Makama,…

Read More