Author: Abdullahi Yusuf

An Kaddamar Da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre Daga Abdullahi Yusuf A ranar Al’hamis din nan ne a ka kaddamar da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre, don bunkasa tattalin arziki da jin dadin mutanen yankin. An yi bikin kaddamarwar ne a Ofishin Shiyyar Arewa Maso Yamma na Cibiyar Koyar da Fasahar Kyankyasa Ta Kasa da ke Farm Centre a Kano. Kungiyar Rayawa da Ci Gaban Al’umma ta Kano,wato KCDS ce ta shirya taron na kwana daya. A cikin jawabinsa, Shugaban Kungiyar ta KCDS, Farfesa Muhammad Tabi’u,ya ce makasudin kaddamar da Kungiyar ta Ci Gaban Tarauni, Daurawa…

Read More

Jam’iyyar ADC Ta Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Sabuwar Dokar Haraji Ta Kasa Daga Abdullahi Yusuf Jam’iyyar ADC ta soki Gwamnatin Tarayya a kan sabuwar Dokar Haraji Ta Kasa,ta na mai cewa dokar za ta kara jefa “Yan Nigeria cikin halin kuncin tattalin arziki da rashin walwala. Wannan suka kuwa na kunshe ne a cikin sakon Barka Da Kirsimati na Jam’iyyar wanda Mataimakin Sakatarenta na tsare-tsare na kasa,Ali Tukur Gantsa,ya rattabawa hannu. A cikin sanarwar dai,Ali Gantsa, tsohon sakataren Jami’yar PDP a jihar Jigawa Kuma sakataren tsare stare shiyar Arewa maso yamma, ya taya mabiya addinin Kirista murnar zagayowar ranar Kirsimati,ya…

Read More