Al’ummar ‘yan jarida a jihar Kano na jimamin rasuwar fitaccen ɗan jarida da ya shahara wajen rahotannin kotu da laifuka, Balarabe Nazeephy, wanda aka fi sani da “Wakilin Kotu da ’Yan Sanda.”
Rahotanni sun ce marigayin ya rasu ne bayan ya shafe sama da shekaru talatin yana aikin jarida, inda ya yi fice wajen rahoto kan harkokin shari’a da tsaro cikin ƙwarewa da jajircewa.
Nazeephy ya samu karɓuwa a tsakanin abokan aikinsa, lauyoyi da jami’an tsaro, sakamakon yadda yake gabatar da rahotanni cikin inganci da gaskiya.
Wani ɗan jarida, Abbas Ibrahim, ya bayyana cewa marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen gina masa ƙwarewa tun yana matashi a gidan rediyon Kano.
Ya ce a wancan lokaci, ana ɗora sababbin ‘yan jarida ƙarƙashin gogaggun ma’aikata domin koyon aiki, inda aka haɗa shi da Nazeephy, wanda ya ba shi horo da jagoranci.
A cewarsa, darasin farko da ya koya masa shi ne muhimmancin jajircewa da dogaro da kai a aikin jarida, har ma suna yawan tafiya a ƙafa zuwa kotu domin samun labarai kai tsaye.
Haka kuma, ya ce marigayin ne ya gabatar da shi ga rahoton kotu, inda ya koya masa yadda ake bin shari’o’i, da kuma yadda ake mutunta dokokin kotu da al’adunta.
Baya ga haka, ya ce Nazeephy ya koya masa muhimmancin kyakkyawar mu’amala da kowa a cikin tsarin shari’a, daga lauyoyi zuwa ma’aikatan kotu, tare da girmama waɗanda ake zargi da laifi.
Abbas Ibrahim ya ce rasuwar ta zo masa da ɗan firgici, bayan da wani abokin aiki ya sanar da shi labarin.
Sai dai ya ce duk da rasuwarsa, gudummawar da marigayin ya bayar ga aikin jarida za ta ci gaba da rayuwa, musamman ta hanyar ‘yan jaridar da ya horar.
Ana dai addu’ar Allah ya jikansa da rahama, ya kuma ba iyalansa da al’ummar ‘yan jarida haƙurin jure wannan rashi.
