Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, January 15
    • Shafin Farko
    • Labarai

      An Kaddamar Da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre

      January 1, 2026
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa

      Jam’iyyar ADC Ta Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Sabuwar Dokar Haraji Ta Kasa

      December 26, 2025
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » ROLAC Ta Shirya Wa “Yan Jarida Da “Yan Fafutuka Taron Koya Dabarun Bibiyar Kasafin Kudin Jihar Kano
    Featured

    ROLAC Ta Shirya Wa “Yan Jarida Da “Yan Fafutuka Taron Koya Dabarun Bibiyar Kasafin Kudin Jihar Kano

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufDecember 9, 2025No Comments1 Views
    IMG 20251209 WA0057
    ROLAC Ta Shirya Wa “Yan Jarida Da “Yan Fafutuka Taron Koya Dabarun Bibiyar Kasafin Kudin Jihar Kano
    Daga Abdullahi Yusuf
    An yi kira ga “Yan Jarida da Kungiyoyin Fafutuka na Jihar Kano da su rika bibiyar Kasafin Kudi na Jihar Kano, domin tabbatar da bin doka da gaskiya wajen aiwatar da shi.
    An yi wannan kiran ne kuwa,a wajen taron koya wa “Yan Jarida da “Yan Kungiyoyin Fafutuka da ke Jihar Kano, dabarun bibiyar aiwatar da Kasafin Kudi na Jihar Kano,a ranar Litinin din nan da ta wu ce.
    Wanda ya gabatar da Makala a wurin taron,Dr.Abdulsalam Kani,shi ya yi wannan kiran,in da ya shawarci mahalarta taron da su yi amfani da Dokokin gudanar da harkokin kudi na Jihar Kano,wato PFMLs,wajen bibiyar Kasafin Kudin.
    Dr.Kani ya ce Kungiyar ROLAC ce ta bayar da taimako wajen saukaka dokokin gudanar da harkokin kudi na Jihar Kano,domin “Yan Jarida da”Yan Kungiyoyin Fafutuka su sami saukin yin amfani da su wajen bibiyar Kasafin Kudi na Jihar Kano domin tabbatar da gaskiya da adalci wajen aiwatar da shi.
    Daga nan sai ya shawarci “Yan Jaridar da su rika amfani da kwarewarsu ta bincike wajen bibiyar Kasafin Kudi na Jihar Kano domin tabbatar da cewa a na aiwatar da shi yadda ya kamata.
    Haka su ma “Yan Kungiyoyin Fafutukar,Masanin ya yi kira a garesu da su rika bibiyar Kasafin Kudin domin tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Kano ta na aiwatar da ayyukan da ya kunsa.
    Sannan kuma,Dr.Kani ya shawarci mahalarta taron da su bibiyi Kasafin Kudin domin su tabbatar da cewa a na sakin kudin da ya kunsa don aiwatar da ayyuka,sannan su hakikance an yi wadannan ayyukan.
    Bugu da kari,Dr.Kani ya yi kira a garesu da su tabbatar da cewa a na gabatar da Kasafin Kudin ga Majalisar Dokokin Jihar Kano a kan lokacin da doka ta tsara,sannan su tabbatar da cewa Kasafin Kudin ya kunshi ra’ayoyin da mutanen Jihar Kano su ka bayar wajen tsara shi.
    Haka kuma ya shawarce su da su halarci Taron Jin Ra’ayin Jama’a wanda Majalisar Dokokin Jihar Kano za ta kirawo domin tattaunawa a kan yadda za a aiwatar da Kasafin Kudi na Jihar Kano na shekarar kudi ta 2026, wadda Maigirma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gabatar mata.
    Dr.Kani ya ce,ya kamata “Yan Jaridar da “Yan Kungiyoyin Fafutukar su bibiyi Kasafin Kudin na Jihar Kano daki-daki,domin su fada wa Gwamnati da Jama’ar Jihar Kano duk wasu matsalolin da su ka gano a cikinsa,domin a gyara domin ci gaban Jihar.
    A cikin jawabinsa, Shugaban Kungiyar ta ROLAC a Jihar Kano,wadda ita ce ta shirya taron,Malam Ibrahim Bello,ya ce an kira taron ne domin a koya wa “Yan Jarida da “Yan Kungiyoyin Fafutuka dabarun bibiyar Kasafin Kudin Jihar Kano domin tabbatar da gaskiya da bin doka wajen aiwatar da shi.
    Shugaban na ROLAC, wanda Isma’il Bello ya wakilta, ya ce kungiyarsa a shirye ta ke ko da yaushe, wajen yin aiki tare da “Yan Jarida da “Yan Kungiyoyin Fafutuka domin tabbatar da bin doka,gaskiya,adalci da rikon amana wajen aiwatar da Kasafin Kudi na Jihar Kano.
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 15, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 14, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 13, 2026
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      By Abdullahi YusufJanuary 15, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU: Da Gwanin rawa ya fadi,sai ya ce,”Wata haka.”

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 14, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 13, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 12, 2026
      © 2026 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.