Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, January 15
    • Shafin Farko
    • Labarai

      An Kaddamar Da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre

      January 1, 2026
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa

      Jam’iyyar ADC Ta Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Sabuwar Dokar Haraji Ta Kasa

      December 26, 2025
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » *LESPADA Ta Bukaci Faɗaɗa Tsarin Gwajin Shan Ƙwayoyi Na Gwamnatin Tarayya Zuwa Makarantu Da Kafin Aure*
    Featured

    *LESPADA Ta Bukaci Faɗaɗa Tsarin Gwajin Shan Ƙwayoyi Na Gwamnatin Tarayya Zuwa Makarantu Da Kafin Aure*

    Abbas IbrahimBy Abbas IbrahimDecember 23, 2025No Comments1 Views
    aeb6093e5d664bb9bfcf15470d50a379

     

    Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da tsarin gwajin shan ƙwayoyi na dole a matsayin sharadi ga duk wanda ke neman aiki a tarayya.

    Masu ruwa datsaki da dama sun bayyana matakin, abun da ya dace domin yaki da shan miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

    Wannan tsari, wanda ya shafi masu neman aiki, na daga cikin kokarin da gwamnati ke yi na karfafa gaskiya, tsaro da kwarewa a cikin hukumomin gwamnati tare da rage barazanar da shan miyagun kwayoyi ke haifarwa.

    Da take martani kan wannan batu, shugabar Kungiyar dake yaki da Shan Miyagun kwayoyi wato , League Of Societal Protection Against Drug Abuse (LESPADA), Ambasada Maryam Hassan, ta yaba wa Gwamnatin Tarayya bisa daukar wannan muhimmin mataki na kare ma’aikata da makomar Najeriya.

    A cewarta, shan miyagun kwayoyi na ci gaba da zama babbar barazana ga iyalai, hukumomi da kuma cigaban kasa baki daya.

    “Mayar da gwajin shan kwayoyi sharadi kafin samun aiki zai taimaka wajen karfafa dabi’a nagari, tabbatar da tsaron wuraren aiki, da samar da ma’aikata marasa shan miyagun ƙwayoyi,” in ji Ambasada Maryam Hassan. “Wannan tsari ba wai na aiki kadai ba ne, illa dai na kare al’umma baki ɗaya.”

    Ta kuma jaddada cewa ya dace a fadada wannan tsari fiye da batun aiki, ta hanyar shigar da shi cikin shigar dalibai makarantun sakandare da na gaba da sakandare, da kuma kafin aure, kamar yadda ake yi wajen gwajin Kwayoyin halitta, wato (genotype) da na lalurar dake karys karkuwan jiki wato HIV.

    “Gano matsala da wuri da kuma daukar matakin gaggawa na iya ceton rayuka, kare iyalai, da hana mummunan tasiri na dogon lokaci,” in ji ta.

    Ambasada Maryam Hassan ta bayyana wannan tsari a matsayin wata alama mai karfi ta kudurin gwamnati na yaki da shan miyagun kwayoyi, tare da kira ga dukkan masu ruwa da tsaki ciki har da cibiyoyin ilimi, kungiyoyin addini, da kungiyoyin farar hula da su mara wa shirin baya tare da tabbatar da dorewarsa.

    Ta kammala da yaba wa Gwamnatin Tarayya bisa yin tsayuwar daka, tana mai cewa hadin kai tsakanin kowa da kowa ne zai haifar da kasa mai lafiya, tsaro, da cigaba mai dorewa.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abbas Ibrahim

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 15, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 14, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 13, 2026
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      By Abdullahi YusufJanuary 15, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU: Da Gwanin rawa ya fadi,sai ya ce,”Wata haka.”

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 14, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 13, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 12, 2026
      © 2026 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.