Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Wednesday, January 14
    • Shafin Farko
    • Labarai

      An Kaddamar Da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre

      January 1, 2026
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa

      Jam’iyyar ADC Ta Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Sabuwar Dokar Haraji Ta Kasa

      December 26, 2025
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » An Kaddamar Da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre
    Labarai

    An Kaddamar Da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufJanuary 1, 2026No Comments2 Views
    IMG 20260101 WA0052(2)

    An Kaddamar Da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre

    Daga Abdullahi Yusuf

    A ranar Al’hamis din nan ne a ka kaddamar da Kungiyar Ci Gaban Tarauni,Daurawa Da Farm Centre, don bunkasa tattalin arziki da jin dadin mutanen yankin.

    An yi bikin kaddamarwar ne a Ofishin Shiyyar Arewa Maso Yamma na Cibiyar Koyar da Fasahar Kyankyasa Ta Kasa da ke Farm Centre a Kano.

    Kungiyar Rayawa da Ci Gaban Al’umma ta Kano,wato KCDS ce ta shirya taron na kwana daya.

    A cikin jawabinsa, Shugaban Kungiyar ta KCDS, Farfesa Muhammad Tabi’u,ya ce makasudin kaddamar da Kungiyar ta Ci Gaban Tarauni, Daurawa Da Farm Centre shi ne domin a samar da tsaro,ci gaban tattalin arziki da walwalar mutanen yankin.

    Tabi’u ya ce, hakan ya zamo dole saboda bullar matsalolin tsaro da su ka hada da sace-sace,kwacen waya,shan kwaya da fyade tsakanin matasa da sauransu, a wadannan unguwannin da makwabtansu.

    Ya ce abin takaici ne ganin cewa Kano da ta shahara wajen kasuwanci, ilimi da al’adu sai ga shi ta na fama da matsalolin tsaro da makamantansu.

    Domin magance wadannan matsaloli, in ji Shugaban,sai a ka kirkiro wannan Gidauniya domin mutane su taimaka da kudi daidai karfinsu.

    Ya ce kowa na iya bayar da abin da ya saukaka,kuma a kowanne lokaci, don cinma burin da a ka sanya a gaba.

    Farfesa Tabi’u ya ce hakan ya zamo dole saboda Gwamnati kadai ba za ta iya biya wa mutane dukkan bukatunsu ba.

    Ya ba da tabbacin cewa duk kudaden da a ka tara a cikin Gidauniyar za a yi amfani da su cikin gaskiya, rikon amana da tsoron Allah.

    Shi ma a cikin jawabinsa,Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sunusi II, ya koka game da yadda a ke samun karuwar shan miyagun kwayoyi a Kano, musamman tsakankanin matan aure da matasa.

    Sarkin, wanda Hakimin Tarauni, Alhaji Bello Bayero, ya wakilta,ya ce wannan abin takaicin ne ya ke jawo yawan aikata laifuka kamarsu fyade,sace-sace,kwacen waya da kisan kai a yankin.

    Saboda haka, Sarkin ya yi maraba da kaddamar da wannan Kungiya, wadda ya ce za ta taimaka matuka wajen magance wadannan matsaloli.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      By Abdullahi YusufJanuary 14, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU: An ce da Kare a na biki a gidansu,ya ce,”In gani…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 13, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 12, 2026

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      January 11, 2026
      © 2026 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.