Author: Abbas Ibrahim

Jam’iyyar African Democratic Party (ADC) ta soki dokar gyaran haraji ta Gwamnatin Tarayya, inda ta bayyana ta a matsayin wadda ke cutar da al’umma tare da barazanar jefa kasar cikin karin matsin tattalin arziki da rashin daidaiton zamantakewa. Jam’iyyar ta kuma nuna damuwa kan ci gaba da tabarbarewar tsaro a sassan kasar, inda ta bayyana cewa halin da ake ciki a matsayin abin tausayi da ke kara haifar da rashin aminci tsakanin jama’a da gwamnati, sakamakon kasa cika alkawuran da aka sha yi na kare rayuka da dukiyoyi. Wadannan batutuwa na kunshe ne a cikin sakon Kirsimeti da jam’iyyar…

Read More

Shugabar Hukumar Kula da Tsarin Kiwon Lafiya na taimakekekiya ta Jihar Kano (KSCHMA), Dakta Rahila Aliyu Mukhtar, ta yi kira da a karfafa hadin gwiwa da shugabannin mata a kungiyoyin kwadago domin fadada wayar da kai da kuma amfanin shirin inshorar lafiya na jihar. Dakta Rahila Mukhtar ta bayyana hakan ne yayin da ta halarci Taron Tsare-tsaren Dabaru na Shugabannin Kwamitin Mata na Ƙungiyoyin Kwadago yayinda taron ke gudana . Duk da cewa ta isa taron ne a tsakiyar shirin, ta gabatar da cikakken bayani kan Tsarin Inshorar Kiwon Lafiya na Jihar Kano, inda ta yi bayani kan ayyukansa,…

Read More

Alhaji Aminu Baba Dan,agundi yace Sanata Rabiu Musa Kwankwaso bashi da wani Hurumi na bada Shawarar Janye Jami’an tsaron Gidan Sarki na Nassarawa Yace “Maganar da take kotu to Kai waye zakayi wannan maganar a Matsayin kana wa?” Sanarwa da Abubakar Balarabe Kofar Na, Isa ya bayar ta ruwaito Amina Babba na cewa  “Baka da wani Hurumi akan wannan, kuma koshi Gwamnan Kano Bashi da wannan Hurumin.” Sarkin Dawaki Babba ya kara da cewa Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero kotu ce ta bashi wannan tsaro ba Gwamnati ba. A don haka ne ma yace wannan maganar da Sanata Rabiu…

Read More

´ Taron jama’a mai yawa ne , safiyar ranar Talata yayi Tururuwa domin halartar jana’izar Muhammad Sani Hassan, wanda aka fi sani da Sanin Kale, a unguwar Yakasai da ke cikin ƙaramar hukumar Municipal. Sanin Kale, wanda bai yi wata rashin lafiya ba, ya rasu ne bayan ya kammala sallar Isha’i. Ƙanwarsa, Zainab Hassan wadda aka fi sani da Ta’annabi, ta bayyana cewa Sani, wanda ya shahara a unguwar, ya yi wasa da yara tare da raba musu alewa kaɗan kafin rasuwarsa. Wani mazaunin yankin, Mohammed Yakasai, ya ce: “A nan kusa bamu ga irin wannan taron jama’a mai yawa…

Read More

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da tsarin gwajin shan ƙwayoyi na dole a matsayin sharadi ga duk wanda ke neman aiki a tarayya. Masu ruwa datsaki da dama sun bayyana matakin, abun da ya dace domin yaki da shan miyagun ƙwayoyi a Najeriya. Wannan tsari, wanda ya shafi masu neman aiki, na daga cikin kokarin da gwamnati ke yi na karfafa gaskiya, tsaro da kwarewa a cikin hukumomin gwamnati tare da rage barazanar da shan miyagun kwayoyi ke haifarwa. Da take martani kan wannan batu, shugabar Kungiyar dake yaki da Shan Miyagun kwayoyi wato , League Of Societal Protection Against…

Read More

Shugaban Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA), Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (rtd), ya jaddada cewa sabon tsarin gwajin miyagun ƙwayoyi da aka kaddamar a makarantu an tsara shi ne domin rage yawaitar shan kwayoyi a tsakanin matasan Najeriya, musamman daliban da ke neman shiga manyan makarantun gaba da sakandare. Ya bayyana cewa tsarin, wanda ya ƙunshi gwaje gwaje na dole da na bazata, mataki ne na kariya ba na hukunci ba, domin hana matasa tsunduma cikin shan miyagun kwayoyi. Marwa ya bayyana hakan ne yayin da ya karbi Zababben Shugaban Jami’ar Taraba dake (TSU), Jalingo,…

Read More

Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato Fiscal Discipline and Development Advocacy (FIDAC) ta yi kira ga kungiyoyin fararen hula (CSOs) da su bayar da muhimmiyar gidunmowa wajen tabbatar da aiwatar da Dokokin Sauye-sauyen Haraji na shekarar 2025 tana mai jaddada cewa nasara ba kawai a wayar da kai take ba akwai bukatar shigo da Al umma A cikin wata sanarwa da shugaban ta, Abdussalam Muhammad Kani, ya fitar ya bayyana sauye-sauyen harajin a matsayin wani mataki na zamanantarwa tare da inganta tsarin haraji na Najeriya,da kuma fadada hanyoyin samar da kudin…

Read More

Mata ashirin da biyar (25) da suka Samu Lafiya daga cutsr yoyon fitsari a Gusau, Jihar Zamfara, sun kammala wani shirin koyon sana’o’i da Gidauniyar Bashir Foundation for Fistula and Women’s Health Rehabilitation ta shirya, domin dawo da mutuncinsu da kuma ƙarfafa su su dogara da kansu. Jagorar shirin, Nafisa Balarabe Abdullahi, ta bayyana cewa an horas da waɗanda suka ci gajiyar shirin a harkokin yin man shafawa (pomade) da kuma yin kayan ado na beads, sannan aka ba su kayan farawa domin su samu damar fara ƙananan sana’o’i. Ta ce shirin, wanda Asusun Majalisar Ɗinkin Duniya kan Yawan Jama’a…

Read More

Rundunar Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun kwayoyi ta kasa dake Kano (NDLEA) ta sake jaddada aniyarta ta kara kaimi wajen yaki da shan miyagun kwayoyi a fadin jihar. Kwamandan Rundunar , CN DY Lawal, ya bayyana hakan ne yayin da yake karbar shugabar kungiyar Kare Al’umma Daga Shan Miyagun kwayoyi (LESPADA), Ambasada Maryam Hassan, a ziyarar ban girma data kaiwa kwamandan. Ya bayyana manyan nasarorin da hukumar ta samu wajen yakar shan miyagun ƙwayoyi, ya jaddada cewa yaki da miyagun kwayoyi alhakin kowa da kowa ne, kuma yana bukatar hadin gwiwar dukkan masu ruwa da tsaki. CN…

Read More

An kammala taron kwana huɗu da asusu majalisar dinkin duniya (UNFPA) ta shirya a hotel din Tahir dake garin kano, kan inganta kyawawan halayen maza, inda mahalarta suka ƙirƙiro tsare-tsare na ayyuka domin magance aurar da ƙananan yara, kaciya ga mata (FGM), da kuma cin zarafin jima’i da na jinsi (SGBV). Mahalarta taron, waɗanda suka fito daga kungiyoyin matasa da na al’umma daban-daban, ana sa ran za su fara aiwatar da ayyukan da aka tsara kafin 31 ga watan Disambar shekarar ta 2025. Da take jawabi a Yayin rufe taron, jami’ar UNFPA Hajiya Bahijja Bello Garko ta tabbatar da kudirin…

Read More